Posts

Showing posts from October, 2020

ASIRIN WASU GWAMNONIN NIGERIA YA TONU

ASIRIN WASU GWAMNONIN NIGERIA YA TONU Zanga-zangar ENDSARS ta bar baya da kura, yanzu sun koma farfasa dakin ajiyar abinci a wasu jihohin Nigeria suna kwasar abinci na tallafin Coronavirus wanda shugaba Muhammadu Buhari ya bawa gwamnanoni domin su rabawa talakawa amma wasu gwamnonin suka ki rabawa Ina tuna lokacin da Ministar jin kai Hajiya Sadiya Umar Farouk ta bada sanarwan cewa gwamnatin shugaba Buhari ta kashe biliyoyin Naira wajen sayan abincin tallafi na Coronavirus, amma a lokacin aka dinga tsine mata ana karyatata cewa ba'a ga abincin ba, ita ma yau Allah Ya wanke ta Ga abinci nan shugaba Buhari ya bayar a baku, amma wasu miyagun gwamnoni sun boye sun barku da jin haushin shugaba Buhari kuna ta zaginsa ya kawo yunwa, gashi nan asirin mugayen gwamnonin ya fara tonuwa Wannan zanga-zangar ENDSARS ta yaye wa masu hankali duhun sharri da aka yiwa shugaba Buhari, yanzu masu hankali sun fahimci gaskiya, hakika shugaba Buhari alheri ne wa Nigeria  Fasa gidan ajiyar abinci na gwamna

Musliman India

  <iframe data-aa="1508985" src="//ad.a-ads.com/1508985?size=728x90" scrolling="no" style="width:728px; height:90px; border:0px; padding:0; overflow:hidden" allowtransparency="true"></iframe> Akasarin Musulan Indiya na aiki a ƙananan ma'aikatun masu ƙananan ƙarfin tattalin arziki a kasar Kusan shekaru 30 da suka gabata duk da shaidu 850, sannan daga bisani fiye da kasidu 7,000 da hotuna da faya-fayen bidiyo da aka gabatar, wata kotu a Indiya ba ta samu kowa da aikata laifin rushewa tare da banka wuta a wani masallacin da aka gina tun a ƙarni na 16 a kasar ba, wanda wasu gungun mutane mabiya addinin Hindu ne suka kai hari a masallacin da ke birnin Ayodya mai daraja. A cikin mutum 32 da ake zargi da yanzu haka suke a raye, akwai tsohon mukaddashin Firimiya LK Advani, da sauran jiga-jigan jam'iyyar BJP. A hukuncin da aka yanke a ranar Laraba, kotuna ta wanke duka waɗanda ake zargin, inda ta ce wasu ne da ba a san ko su